IQNA

Babban Limamin Ghana Ya Bukaci Mutane Da Su Yi Bukukuwan Salla A Gida

22:56 - July 25, 2020
Lambar Labari: 3485018
Tehran (IQNA) babban limamin kasar Ghana ya bukaci musulmi da suka gudanar da bukukuwan salla babba a cikin gidajensu.

Shafin yada labarai na My Joy Online ya habarta cewa, a cikin wani bayani da ya fitar, Sheikh Usman Nuhu Sharubutu babban limamin kasar Ghana ya bukaci musulmi da suka gudanar da bukukuwan salla babba a cikin gidajensu domin kaucewa kamuwa da cutar corona.

Malamin ya bayyana hakan en a cikin bayanin da mai magana da yawunsa ya fitar, ida ya bayyana cewa ya zama wajibi jama’a su kiyaye dukkanin ka’idojin da aka gindaya domin kare kai daga kamuwa da cutar corona ko kuma yada ta.

Ya cea  kan wannan dalilin en ma aka dakatar da gudanar da abubuwa da dama, da suka hada har sallar jam’i da kuma wasu taruka da kuma halartar makarantu.

A ranar 31 ga wata Yuli ne dai za  agudanar da babbar salla a kasar Ghana.

3912303

 

captcha