Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran SAFA cewa, an fara gudanar da gangamin a yau a dukkanin yankunan Palastinawa da suke karkashin mamayar yahudawan Isra’ila tun daga shekara ta 1948.
Daya daga cikin malamai masu gwagwarmaya a Palastinu Sheikh Ra'id Salah na daga cikin wadanda suke jagorantar wannan gangami a gabashin masallacin Aqsa, kamar yadda a sauran yankunan gabar yamma da kogin Jordan ma Palastinawa suna gudanar da wannan gangami.
Babbar manufar hakan ita ce tabbatar wa yahudawan Isra’ila da cewa Palastinawa ba za su taba amincewa da mamayar da aka yi ma kasarsu tare da kafa Isra’ila ba.
Masu gangamin sun yi ta rera taken neman ‘yanci da Allawadai da mamayar Isra’ila a kan kasarsu, da kuma yin kira ga sauran al’ummomin duniya da su mara baya ga al’ummar palastinu da ake zalunta tsawon tarihin wannan karni.