Cibiyar hubbaren Husani ce take daukar nauyin shiryawa da kuma gudanar da irin wanan horo. Sulaiman Widrago daraktan kula da shirya tarukan kur’ani na wannan cibiya akasar Burkina Faso yabbayan cewa, shirin ya samu nasara matuka, domin kuwa ana samun halartar jama’a musamman ma matasa daga cikinsu.
Shi ma a nasa bangaren Sheikh Abbas Diiyagiti, daya daga cikin malaman da suke koyarwa a wannan wuri, ya bayyana cewa an samu ci gaba matuka, kuma a halin yanzu shirin zai ci gaba da gudana rana guda a cikin kowane mako.