Umar ta rubuta a shafinta na yanar gizo na Facebook cewa, direban ya bayyana ta a matsayin 'yar ta'adda ta kungiyar daesh, yana mai yi mata barazana da cewa zai iya halaka ta.
Tun bayan da aka zabi Trump a matsayin shugaban kasar Amurka, kyamar musulmi da kuma yi musu barazana kan rayuwarsu ke ci gaba da karuwa a dukkanin yankunan kasar, inda musulmia halin yanzu ke rayuwa cikin halin rashin tabbasa a Amurka.